
NAJERIYA, wadda ke alfahari da kanta a matsayin kasa mai karfi a fannin kwallon kafa, na ci gaba da fuskantar abin damuwa a bangaren alkalanci a matakin kasa da kasa. A karo na baya-bayan nan, an sake barin alkalanta a wajen gasar cin kofin duniya ta FIFA World Cup, bayan irin wannan watsi da aka yi musu a gasar AFCON, inda babu ko daya daga cikinsu cikin jerin alkalai 73 da aka zaba.
WANNAN ci gaba da watsi da alkalai ‘yan Najeriya ba wai abin da ya faru kwatsam ba ne, illa wata alama ce ta matsaloli masu zurfi a tsarin tafiyar da kwallon kafa a kasar, musamman a fannin horarwa, tantancewa da kuma bunkasa alkalai. Wannan lamari ya nuna cewa akwai gibi mai girma da ke bukatar gyara cikin gaggawa idan har ana son ganin Najeriya ta dawo kan sahun manyan kasashen da ke taka rawar gani a harkar.
KWALLON kafa ba ta tsaya ga bajintar ‘yan wasa a fili kadai ba. Tana bukatar ingantattun alkalai masu gaskiya da kwarewa da za su tabbatar da an bi dokokin wasa yadda ya kamata. Idan aka ci gaba da ganin cewa alkalai ‘yan Najeriya ba sa samun damar shiga manyan gasa, hakan na haifar da tambayoyi masu tsauri kan ingancin tsarin da ake bi a gida wajen horar da su.
A cewar hukumar FIFA, zabin alkalai na gasar World Cup ya dogara ne kan tsarin “inganci a gaba”, inda aka dade ana bibiyar alkalai tsawon shekaru uku kafin a tantance su. An mayar da hankali kan yadda suke gudanar da ayyukansu a lig-lig na cikin gida, gasa na nahiyar da kuma sauran shirye-shiryen FIFA. Daga cikin alkalai 170 da aka zaba daga sassa daban-daban na duniya, babu ko guda daga Najeriya.
BABBAN jami’in kula da alkalanci na FIFA, Pierluigi Collina, ya tabbatar da cewa wadanda aka zaba su ne mafi nagarta a duniya, inda ya bayyana cewa an zabe su ne daga jerin manyan alkalai da aka dade ana sa ido a kansu. Wannan bayani, ko da yake yana nuna tsarin gaskiya na FIFA, ya zama gargaɗi ga hukumomin kwallon kafa na Najeriya.
IDAN inganci da daidaito ne ma’aunin zabe, to hakan na nuni da cewa Najeriya na fuskantar gazawa a fannin samar da alkalai masu iya taka rawar gani a matakin duniya. Wannan matsala ba ta takaita ga mutum daya ko biyu ba, illa gazawar tsarin gaba daya da ke kula da horarwa, tantancewa da kuma ci gaban alkalai.
A cikin gida kuma, gasar NPFL wadda ya kamata ta zama matattarar horar da alkalai masu kwarewa, ta dade tana fama da matsaloli kamar rashin ingantaccen hukunci, rashin gaskiya da kuma zarge-zargen son zuciya. Wadannan matsaloli na rage kwarin gwiwar masu kallo da kuma lalata martabar alkalai da ke fitowa daga wannan mataki.
IDAN alkalanci a cikin gida na cike da cece-kuce da rashin tabbas, yana zama da wahala kungiyoyin kasa da kasa kamar FIFA da CAF su amince da irin wadannan alkalai a manyan wasanni. Wannan shi ne dalilin da ke kara bayyana dalilin da ya sa ake ci gaba da watsi da su a matakin duniya.
BAYA ga abin kunya da hakan ke haifarwa, akwai kuma babbar illa ta dogon lokaci. Rashin wakilcin alkalai ‘yan Najeriya a manyan gasa na hana su samun kwarewa, gogewa da kuma damar koyo daga manyan alkalai na duniya. Hakan kuma na rage daraja da tasirin Najeriya a fagen kwallon kafa ta duniya.
DON magance wannan matsala, akwai bukatar a dauki matakai masu zurfi da tsari. Hukumar NFF dole ta zuba jari a horar da alkalai ta zamani, ta tabbatar da ana duba lafiyarsu da kwarewarsu akai-akai, tare da shigar da fasahar zamani irin su VAR cikin gasar cikin gida domin inganta alkalanci.
HAKA kuma, dole ne a samar da tsarin tantance aiki mai gaskiya da adalci, wanda ba zai bar son zuciya ko dangantaka ta yi tasiri wajen daukar mataki ba. Hakan zai taimaka wajen gina sabon tsarin alkalanci mai inganci da amincewa.
MASU gudanar da lig kuma suna da muhimmiyar rawa wajen dawo da martaba. Inganta yadda ake shirya wasanni, tsaurara hukunci kan kura-kurai, da kuma inganta jin dadin alkalai zai taimaka wajen samar da yanayi mai kyau da zai inganta aikinsu.
NAJERIYA ba za ta iya ci gaba da murnar nasarorin da take samu daga ‘yan wasa kawai ba, tana barin sauran muhimman bangarori na kwallon kafa. Rashin alkalanta a manyan gasa alama ce karara cewa akwai bukatar cikakken gyara a tsarin gaba daya.
IDAN har ana son Najeriya ta dawo da martabarta a idon duniya, dole ne a mayar da hankali ba kawai kan ‘yan wasa ba, har ma da horar da alkalai masu inganci da za su iya tsayawa da kafar sauran takwarorinsu a duniya. Har sai an yi hakan, wannan matsala za ta ci gaba da zama abin kunya da kuma kira mai karfi na gyara.
