Wednesday, June 17, 2026
  • #201 (no title)
  • About Us
  • Advertise With Us
  • Advertising Services
  • Contact Us
  • Privacy Policy
No Result
View All Result
The Nigeria Standard
SUBSRCIBE
  • Home
    • #201 (no title)
  • News
    • Middle-Belt
    • World
  • Business
    • Entrepreneurship
  • Politics
  • Science & Tech
    • IT
  • Sports
  • Opinion
    • Columns
  • Editorials
  • Lifestyle
    • Culture
    • Travel
  • ‘Yancin Dan Adam
The Nigeria Standard
Home Yancin Dan Adam

Ƙungiyoyin Berom na neman gwamnati ta maido da ‘yan gudun hijira gidajensu

by The Nigeria Standard
April 28, 2026
in Yancin Dan Adam
Reading Time: 3 mins read
0 0
Berom coalition demands return of displaced communities to ancestral lands
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga SEKYEN WALSHAK

Ƙungiyar Berom Diaspora Coalition (BDC) tare da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi sun bayyana damuwa kan ci gaba da tashe-tashen hankula a Jihar Filato, inda suka yi kira ga gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa domin kwato ƙasashen kakanni da kuma sake tsugunar da al’ummomin da aka raba da muhallansu.

A wata taron manema labarai da aka gudanar a Jos, shugaban ƙungiyar kuma mai shirya taron, Barnabas Dazam, tare da BECO, BYM, BEC da BEWDA, ya ce ci gaba da hare-hare kan al’ummar Berom da sauran kabilu ya ƙara ta’azzara matsalar jinƙai a jihar da yankin Middle Belt.

Da yake magana a kan taken, ‘Reclaiming Our Lost Ancestral Lands and Resettlement of Our People’, Dazam ya tunatar da taron da suka yi a baya a ranar 12 ga Nuwamba, 2025, inda suka yi gargadi kan kisan gilla da korar jama’a daga muhallansu.

Ya ce daga Nuwamba 2025 zuwa Afrilu 2026, an kashe sama da mutane 500, yayin da wasu da dama suka jikkata, tare da lalata dukiya mai darajar miliyoyin naira a hare-hare daban-daban.

Ya ce an samu hare-hare a Barakin Ladi, Riyom, Jos South, Bokkos, Bassa da wasu sassan Jos North, ciki har da harin Angwan Rukuba na 29 ga Maris wanda ya kashe sama da mutane 30.

Dazam ya nuna damuwa cewa duk da gargadin da aka yi a baya, hare-hare na ci gaba a yankuna kamar Fan, Heipang, Kassa, Jol, Shonong, Gyel da Danwal, inda aka lalata gonaki tare da raba mutane da gidajensu.

Ya yi zargin cewa sama da ƙauyuka 70 na Berom sun fuskanci matsala, inda aka tilasta wa mazauna barin gidajensu, yayin da wasu ke zargin cewa an mamaye ƙasashensu.

Ya kuma ambaci Mahanga a ƙaramar hukumar Riyom a matsayin wuri da wasu ƙungiyoyi ke dangantawa da maboyar masu aikata hare-hare.

Ya koka da lalacewar gonaki da kuma yadda yankuna suka zama kufai, yana mai maimaita cewa ana ci gaba da raba mutane da muhallansu.

Dazam ya yi tambaya kan yadda hukumomin tsaro ke aiki, yana zargin jinkiri wajen bin bayanan sirri da kuma rashin daidaito a kama masu laifi.

Duk da jinjinawa ga Shugaba Tinubu da Gwamna Mutfwang bisa alkawuran kawo zaman lafiya, ya ce har yanzu ba a ga sauyi mai kyau a fili ba.

Ya bukaci a gudanar da cikakken bincike, a gurfanar da wadanda ake zargi tare da biyan diyya ga wadanda abin ya shafa.

Ƙungiyar ta kuma ƙara jaddada bukatar kafa ‘yan sandan jiha a matsayin mafita ga matsalolin tsaro.

A ƙarshe, Dazam ya roƙi ƙasashen waje da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da su shiga tsakani wajen kawo ƙarshen rikici da kuma taimakawa wajen mayar da ‘yan gudun hijira gidajensu.

Ya ce, “Tsaron al’umma ya kamata ya zama fifiko, ba wai amsa bayan faruwar hari ba.”

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Facebook Twitter Youtube RSS

Subscribe to Weekly Newsletter for New Updates

Check News by Category

Not So Recent News

Important Links

  • About Us
  • Contact Us
  • Advertise With Us
No Result
View All Result

© 2025 The Nigeria Standard - Digital Media

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • #201 (no title)
  • About Us
  • Advertise With Us
  • Advertising Services
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Subscribe

© 2025 The Nigeria Standard - Digital Media