Monday, September 14, 2026
  • #201 (no title)
  • About Us
  • Advertise With Us
  • Advertising Services
  • Contact Us
  • Privacy Policy
No Result
View All Result
The Nigeria Standard
SUBSRCIBE
  • Home
  • News
    • Middle-Belt
    • World
  • Business
    • Entrepreneurship
  • Politics
  • Science & Tech
    • IT
  • Sports
  • Opinion
    • Columns
  • Editorials
  • Lifestyle
    • Culture
    • Travel
  • ‘Yancin Dan Adam
The Nigeria Standard
Home Yancin Dan Adam

Plateau zai tura maniyyata 1,134 zuwa Hajji, an naɗa Idris Wase Amirul Hajj

by The Nigeria Standard
May 4, 2026
in Yancin Dan Adam
Reading Time: 2 mins read
0 0
Plateau to airlift 1,134 Muslim pilgrims, Mutfwang urges discipline, unity
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga PETER TITLE

Gwamnan Jihar Plateau, Barista Caleb Mutfwang, ya yi kira ga maniyyatan Musulmi na jihar da su kasance jakadu nagari yayin da suke shirin tafiya aikin Hajji na bana a birnin Makka na ƙasar Saudiyya.

Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin da yake yi wa maniyyatan bankwana a hedikwatar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Plateau da ke Lamingo Road, inda ya samu rakiyar mambobin Majalisar Zartarwa ta Jiha.

Gwamna Mutfwang ya bayyana cewa jimillar maniyyata 1,134 daga Jihar Plateau za su halarci aikin Hajjin shekarar 2026.

Ya bayyana cewa 570 daga cikinsu gwamnati ce ta dauki nauyin su, yayin da 564 kuma suka biya da kansu.

Yayin bankwana da tawagar, gwamnan ya shawarce su da su kiyaye kyakkyawan sunan Jihar Plateau, yana mai tunatar da irin kyakkyawan hali da maniyyatan jihar suka nuna a shekarar da ta gabata.

Ya kuma bukace su da su ɗauki aikin ibadar da muhimmanci domin su dawo gida a matsayin masu kawo sauyi mai kyau a cikin al’ummominsu.

Gwamna Mutfwang ya kuma sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar.

Ya yi kira ga waɗanda ya kira “masu cin moriyar rikici” da su guji duk wani aiki da ka iya kawo cikas ga zaman lafiya da ci gaban jihar.

A nasa jawabin, Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Plateau (MPWB), Alhaji Dayyabu Dauda, ya yabawa gwamnan kan goyon bayan da yake bai wa hukumar.

Ya gode masa kan samar da ofishi na dindindin da kuma motar gudanarwa, yana mai cewa hakan ya ƙara inganta ayyukan hukumar.

Dauda ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnati wajen tabbatar da sauƙaƙa tafiyar aikin Hajji ga maniyyata daga jihar.

Gwamnan ya kuma naɗa Alhaji Idris Wase a matsayin Amirul Hajj wanda zai jagoranci tawagar Jihar Plateau zuwa aikin Hajjin shekarar 2026.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Facebook Twitter Youtube RSS

Subscribe to Weekly Newsletter for New Updates

Check News by Category

Not So Recent News

Important Links

  • About Us
  • Contact Us
  • Advertise With Us
No Result
View All Result

© 2025 The Nigeria Standard - Digital Media

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • #201 (no title)
  • About Us
  • Advertise With Us
  • Advertising Services
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Subscribe

© 2025 The Nigeria Standard - Digital Media