
Jagoran Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya yi watsi da zarge-zargen da ke cewa ’yan majalisar tarayya ne ke kayyade alawus-alawus dinsu da kansu.
Ya ce a maimakon haka, Hukumar Tattara Kudaden Shiga da Rabon Kudi ta Kasa (RMAFC) ce ke kayyade albashi da kuma kudaden motocin aiki na mambobin Majalisar Dokoki ta Kasa.
Bamidele ya bayyana haka ne yayin da yake mayar da martani kan hukuncin wata kotu da ta ayyana kashe Naira biliyan 110 wajen sayen motocin alfarma (SUV) da kuma biyan alawus-alawus ga ’yan majalisar a matsayin abin da ya saba wa doka.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tuna cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Legas ta kwanan nan ta ayyana tsarin kashe kudaden da Majalisar Dokoki ta Kasa ta yi wajen sayen motoci da biyan alawus-alawus a matsayin wanda ya sabawa doka.
Kotun ta yanke hukuncin cewa kashe Naira biliyan 40 wajen sayen motoci 465 ga ’yan majalisar da kuma Naira biliyan 70 da aka ware a matsayin tallafin alawus ga sabbin mambobin majalisar ya karya dokokin saye da bayar da kwangila, tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma amanar jama’a.
Har ila yau, kotun ta umarci Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, da su tabbatar da cewa duk wasu saye-saye ko kashe kudaden gwamnati da Majalisar Dokoki ta Kasa za ta yi a gaba sun bi dukkan ka’idojin da suka dace.
Sai dai Bamidele ya kare alawus-alawus da ake bai wa ’yan majalisar, yana mai cewa ba su da ikon kayyade albashi ko alawus-alawus dinsu da kansu.
A cewarsa, har yanzu akwai rashin fahimta a tsakanin ’yan Najeriya da dama saboda ba su da cikakken bayani kan yadda ake tsara albashi da alawus-alawus na ’yan majalisa.
Jagoran majalisar ya ce RMAFC ce ke kayyade albashi da alawus-alawus na ’yan majalisa, ba su da hannu wajen yin hakan.
Ya ce, “’Yan majalisa ba su ne ke kayyade albashi da alawus-alawus dinsu ba. Hukumar RMAFC ce ke yin hakan.”
Bamidele ya bayyana cewa kudaden da ake warewa domin motocin aiki da sauran alawus-alawus an fi bayar da su ne domin taimaka wa ’yan majalisa wajen gudanar da ayyukansu na wakilci a mazabunsu da kuma ayyukan dokoki, ba domin amfanin kansu ba.
Ya kuma yi kira da a kara bayyana gaskiya game da albashi da alawus-alawus na masu rike da mukaman gwamnati, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen kawar da rashin fahimta tare da kara wayar da kan jama’a.
(NAN)
